Saturday

Home LABARI DA DUMI DUMI: Shugabar Mata 'Yan Shi'a Ta Fita Daga Shi'a.




Rahotanni daga Lardin jihar Arewa mai nisa ta 'kasar Kamaru. na cewa.
Jagorar mata mabiya akidar Shi'a ta jagoranci wata 'karamar tawaga mai 'kunshe da mata kimanin 7 ciki hada sakatariyar 'kungiyar inda suka yi taron manema labarai suka kuma bayyana cewa sun fita daga shi'a.

"Hajjiya Balkissou Mammane" ita ce shugabar matan a Lardin Arewa mai nisa kuma ta umarci sakatariyar 'kungiya mai suna "Murjannatou Soulyeman" da-ta karanto sanarwar a gaban manema labarai tare da sauran wadanda suka fita daga shi'ar.

KU KARANTA :- Shugaba Buhari ya kafa tarihin a yau, ku karanta dalilai 3


Sai dai sakatariyar ta bayyana cewa ba dawowar da shugaban Najeriya "Muhammadu Buhari" ya yi ce tasa suka fita daga shi'a ba a'a kawai sun fuskanci cewa uwar kungiyar a Najeriya ba-ta mutunta muradunsu shi yasa suka yanke shawarar ficewa daga 'kungiyar inda ta 'kara da cewa za su gudanar da addinin Musulunci babu ruwansu da bin wata akida.




No comments:
Write Comments