Wednesday

Home › › Bayan fitowa daga gidan yari, Sadik Zazzabi ya yo aman wuta (Karanta)




Fitaccen mawakin Hausar nan, Sadik Zazzabi ya ce siyasa ce ta sanya har ya yi zaman gidan kaso na 'yan kwanaki.

Hukumar Tace Fina-finai ta jihar Kano ce dai ta kai mawakin kara gaban kuliya bisa tuhumar sakin wata waka ba tare da iznin hukumar ba, abin da kuma ya kai ga har ya zauna a gidan yari.

Sai dai kuma bayan fitowarsa daga gidan na yari, Zazzabi ya ce wakar ba ta fita ba kuma ya mika ta gaban hukumar domin tantancewa.
Hukumar, wacce Ismaila Afakallahu ke jagoranta dai, ta ce mawakin ya kaddamar da wakar kafin hukumar ta ba shi iznin wallafawa bayan da ya gabatar mata da ita.

A baya dai Sadiq ya shaida wa jaridar Premium Times cewa an kama shi ne saboda yana goyon bayan tsohon gwamnan jihar, Rabiu Musa Kwankwaso wanda ba sa ga maciji da gwamna mai ci, Abdullahi Umar Ganduje.

DANNA NANDON SAUKE VIDEO n





No comments:
Write Comments